Gwamnonin arewa maso yammacin kasar nan na gudanar da taro kan inganta tsaro a Katsina - NAIJA STICK

Mobile Menu

Powered by Blogger.

Top Ads

More News

logoblog

Gwamnonin arewa maso yammacin kasar nan na gudanar da taro kan inganta tsaro a Katsina

Jun 25, 2024


Gwamnonin arewa maso yammacin kasar nan na gudanar da taro kan inganta tsaro a Katsina.

 

Hukumar raya ƙasashe ta majalisar dinkin duniya ke shirya taron wanda ake fatan fito da hanyoyin da za a kawo karshen matsalar tsaro a yankin.


Cikin masu halartar taron har da mataimakin shugaban kasa Khashim Shatima da manyan jami’an tsaro da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.


Taron na kwana biyu na da nufin inganta tsaro a yankin arewa maso yammacin Najeriya kuma zai mayar da hankali ne, wajen samun hadin gwiwar gwamnatocin yankin don tsare al’umma da sana’o’i.